Powerful Hausa Worship Song.mp4 // 1KOR 15. -  Tashin Almasihu daga Matattu1A yanzu kuma, 'yan'uwa, zan tuna muku da bisharar da na sanar da ku, wadda kuka karɓa, wadda kuke bi, 2wadda kuma ake cetonku da ita, muddin kun riƙe maganar da na sanar da ku da kyau, in ba sama sama ne kuka gaskata ba.3Ish 53.5-12 Jawabi mafi muhimmanci da na sanar da ku, shi ne wanda na karɓo, cewa, Almasihu ya mutu domin zunubanmu, kamar yadda Littattafai suka faɗa,  4Zab 16.8-10; Mat 12.40; A.M 2.24-32 cewa an binne shi, an ta da shi a rana ta uku, kamar yadda Littattafai suka faɗa,  5Luk 24.34; Mat 28.16,17; Mar 16.14; Luk 24.36; Yah 20.19 ya kuma bayyana ga Kefas, sa'an nan ga sha biyun. 6Sa'an nan ya bayyana ga 'yan'uwa fiye da ɗari biyar a lokaci guda, yawancinsu kuwa suna nan har zuwa yanzu, amma waɗansu sun yi barci.  7Sa'an nan ya bayyana ga Yakubu, sa'an nan ga dukan manzanni.  8A.M 9.3-6 Daga ƙarshen duka ya bayyana a gare ni, ni ma da nake kasasshe, marar cancanta.  9A.M 8.3 Don ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban ma isa a ce da ni manzo ba, saboda na tsananta wa Ikkilisiyar Allah.  10Amma saboda alherin Allah na zama yadda nake, alherin da ya yi mini kuwa ba a banza yake ba. Har ma na fi kowannensu aiki, ba kuwa ni ba, alherin Allah ne da yake zuciyata.  11To, ko ni ne dai, ko kuma su ne, haka muke wa'azi, ta haka kuma kuka gaskata.