Shin za a yi zabe a wasu kauyukan karkarar kuwa a zaben 2023?
Ta'addanci dai ya yi kakagida a jihohin Kaduna, Katsina, Neja da Zamfara.
Ganin cewa an sami karancin yin rajistar katin zabe a wadannan yankuna, wasu kungiyoyi masu zaman kansu ne ke taimakawa wasu yankunan karkara yin rajistar katin zaben.
Shirin Najeriya a yau ya tattauna da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC, da kungiyoyi masu rajin kare hakkokin jama'a, da masana a kan wannan al'amari.